Polaroid
Uzairu badamasi

BARKA DA ZUWA SHAFI MAI ALBARKA

Alhamdulillah muna muku albishir insha Allah zamu dawo aiki gadan gadan!


Shafin farko

Haidar Ali

Hadisan Manzon Allah (S.A.W.A)




قال رسول الله صلّى الله عليه و آله : مَن أصلَحَ فيما بَينَهُ وبَينَ اللهِ أصلَحَ اللهُ فيما بَينَهُ وبَينَ النّاسِ.

Manzon Allah (S.A.W) ya ce : Duka wandaya gyara tsakaninsa da Allah to Allah zai gyara masatsakaninsa da mutane.

قال رسول الله صلّى الله عليه و آله: خَفِ اللهَ كَأَنَّكَ تَراهُ فَإِن كُنتَ لاتَراهُ فَإِنَّهُ يَراكَ .

Manzon Allah (S.A.W) ya ce : Ka ji tsoron Allah kamar kana ganinsa idan ka kasance ba ka ganinsaai shi yanaganinka.

قالت فاطمه زهراعليها السّلام: مَن أصعَدَ إلَى اللهِ خالِصَ عِبادَتِه ِأهبَطَ اللهُ إلَيهِ أفضَلَ مَصلَحَتِه

FatimatuzZahra (AS) tana cewa : Duk wandaya kusanta da Allah yana maitsarkake ibadarsa Allah zai saukar masada mafificiyar maslaharsa (ya biya masa mafificiyarbukatarsa)


قال رسول الله صلّى الله عليه و آله: لَو اُتِيتُ بِشابٍّ مِن شَبابِ الشِّيعَةِ لا يَتَفَقَّهَ (في الدِّينِ) لَأَدَّيتُهُ .

Manzon Allah (S.A.W) ya ce : Da za a zomun da wanisaurayi daga samarin shi’a dabaya nemanilimin addini da na ladabatarda shi.

قال رسول الله صلّى الله عليه و آله: فَضلُ الشّابِّ العابِدِ الَّذي تَعَبَّدَفي صِباهُ عَلَى الشَّيخِ الَّذي تَعَبَّدَبَعدَ ما كَبُرَت سِنُّهُ كَفَضلِ المُرسَلينَ عَلى سائِرِ النّاسِ.

Manzon Allah (S.A.W) ya ce : Fifikon saurayi maiibada wanda yake bauta a kuruciyarsaakan tsohon da yake bautabayan ya manyanta kamar fifikonmanzanni ne akan sauran mutane.

قال رسول الله صلّى الله عليه و آله: إنَّ اللهَ يُحِبُّ الشّابَّ الَّذي يُفنيشَبابَهُ في طاعَةِ اللهِ عزّوجلّ

Manzon Allah (S.A.W) ya ce : Allah yana son bawan da yakekarar da samartakarsa wajan bin (bautar) Allah (SWT) .

قال رسول الله صلّى الله عليه و آله: إنَّ الله تَعالى يُباهي بِالشّابّ ِالعابِدِ المَلائِكةَ ، يَقولُ : اُنظُرُواإلى عَبدي! تَرَكَ شَهوَتَهُ مِن أجلي .

Manzon Allah (S.A.W) ya ce : Allah yana alfahari da saurayimai bauta ga mala’iku , yana cewa : ku duba bawana! ya bar sha’awarsasaboda ni.

قال امام صادق عليه السّلام: قالَ رسولُ اللهِ صلّى الله عليه و آله : ليسَ مِنّي مَنِ استَخَفَّ بِالصَّلاةِ ، لايَرِدُ عَلَيَّ الحَوضَ لا وَاللهِ .

Manzon Allah (S.A.W) ya ce : Wanda ya wulakanta salla ba ya dagacikinmu, ba kuma zai zotafkina ba , a’a sam Wallahi!.

قال رسول الله صلّى الله عليه و آله: النَّظَرُ في وَجهِ العالِمِ حُبّاً لَهُ عِبادَةٌ .

Manzon Allah (S.A.W) ya ce : Duba zuwa ga fuskar malamidomin so a gare shi ibada ne.

قال رسول الله صلّى الله عليه و آله: خَيرُ النّاسِ منِ انتَفَعَ بِهِ النّاسُ

Manzon Allah (S.A.W) ya ce : Mafificin mutane wanda mutane suka amfana dashi.

قال رسول الله صلّى الله عليه و آله: إنَّ أبخَلَ النَّاسِ مَـن بَخَلَ بـِالسَّـلامِ .

Manzon Allah (S.A.W) ya ce : Hakika mafi rowarmutane shi ne wanda yayi rowa dasallama.

قال رسول الله صلّى الله عليه و آله: لينوا لِمَن تُعَلِّمون َولِمـَن تَتَعَلـَّمـونَ مِـنـهُ .

Manzon Allah (S.A.W) ya ce : Ku tausasawa wanda kukekoyarwa da kuma wanda kukekoya daga gare shi.

قال رسول الله صلّى الله عليه و آله: أحسِن إلى مَن أساءَ إلَيكَ .

Manzon Allah (S.A.W) ya ce : Ka kyautata wa wandaya munana maka.

قال رسول الله صلّى الله عليه و آله: المُسلِمُ مَن سَلِمَ المُسلِمونَ مِن لِسانِهِ ويَدِهِ .

Manzon Allah (S.A.W) ya ce : Musulmi shi ne wanda musulmi suka kubuta dagaharshensa da hannunsa.

قال رسول الله صلّى الله عليه و آله: إنّي أمزَحُ ولا أقولُ إلّا حَقاً .

Manzon Allah (S.A.W) ya ce : Ni inayin raha amma ba na fadasai gaskiya.

قال رسول الله صلّى الله عليه و آله: النَّظَرُ سَهمٌ مَسمومٌ مِن سِهامِ إبليسَ فَمَن تَرَكَها خَوفاً مِنَ اللهِ أعطاهُ إيماناً يَجِدُ حَلاوَتَهُ في قَلبِهِ .

Manzon Allah (S.A.W) ya ce : Kallo (zuwa gaharam) kibiya ce daga kibiyoyin Iblis duk wanda yabar shi saboda jin tsoron Allah, zai ba shi imanin dazai ji dadinsaa zuciyarsa.

قال رسول الله صلّى الله عليه و آله: إنَّ اللهَ تَعالىيُحِبُّ الشّابَّ التّائِبَ .

Manzon Allah (S.A.W) ya ce : Allah yanason saurayi mai tuba.

قال رسول الله صلّى الله عليه و آله: اِعمَل لِدُنياكَ كَأنَّكَ تَعيشُ أبَداً ، وَاعمَل لِآخِرَتِكَ كَأَنَّكَ تَموتُ غَداً.

Manzon Allah (S.A.W) ya ce : Ka yi aiki don duniyarka kamar ka rayu harabada, ka yi aiki don lahirarka kamar ka mutu gobe.

قال رسول الله (ص) : خير لهو المؤمن السباحة ، وخير لهو المرأَة المغزل

Manzon Allah (S.A.W) ya ce : Mafificin wasan mumini shi ne iyoa ruwa, mafificin wasan mace shi ne saka.



.
Copyright © 2018~2022.
( Uzairu Badamasi Sufi )
Harkarmusulunci@yahoo.com
All rights reserved

Bamu Da Alhakin Tallar Da Ake Sawa Akan Wannan Website Din